2

7.2K 429 4
                                    

          🤰
   CIKI DA GASKIYA.......!!
           {🔪wuk'a bata hudashi🗡}

         Bilyn Abdul ce🤙🏻

NIKA'DAI WRITER ASSO.......😜

Sadaukarwa
     My sweet dady
            (ALLAH ya gafarta maka)🤲🏻

2⃣

     Bak'aramin kuka Aysha tasha ba,  hakama mamanta tayi kukan a 6oye, fadeelama tasha kuka Dan za'a rabata da 'yan k'annenta masu d'ebe kewarta,  amma babu yanda zatayi, Dan dolene kowa yabi umarnin k'anin mahaifin nasu, Wanda ayanzu ya maye musu gurbin mahaifi agaresu, tunda basuda kamarsa.

Tunda safe gwaggo Asma'u tawuce da Abba katsina, (a can take aure).
   Hakama uncle Ahmad yawuce da Ummulkhairi Jigawa wajen aikinsa (shima iyalinsa nacan).
    Itakam Aysha sai zuwa gobe idan ALLAH yakaimu da safe zasu wuce da gwaggo bintu zuwa Abuja.

_______________________
       Washe gari

(Sabuwar rayuwa)

           Haka Ai'sha tatashi sukuku kasancewar kuka datasha itada fadeelah yayarta a daren jiya, haka sukaita kuka har saida mama ta tsawatar musu, daga baya kuma tayi musu nasiha da nuna musu muhimmancin hak'uri da yarda da k'addara, tak'arashe dayima Aysha nasiha akan takare mutuncinta a bak'on muhallin dazata tsinci kanta.
    Kada ta kasance mai kwad'ayi da shiga sabgar da babu ruwanta, banda rashin kunya ganagaba da ita, takuma ringa yima gwaggo bintu biyayya amatsayinta na k'anwar mahaifinta, kada tasake wani yarud'eta ya lalata mata tarbiyyar dasuka gina tsawon shekara 13, koda kuwa a yaran gidanne, tarik'e addininta kada tazama mai sakaci dashi, takula sosai.
      Nasihar mama tashigi Aysha, kuma ta kar6a cikin kuka da alhinin rabuwa da mahaifiyar tasu, wadda tunda tayi wayau basu ta6a rabuwaba koda na kwana d'aya, Dan marigayi baya barinsu zuwa ko ina Hutu, indai ziyara tawuce ta wuni d'aya basa zuwanta.

Haka suka kwana Aysha na kwakume da mama har asubahi, bayan sunyi sallar Asuba gwaggo bintu tashigo tace Aysha tashirya dan sotake su Isa da wuri.
    Itadai mama batace uffanba, tana zaune tana lazimi, Aysha tamik'e tana shiri tana kuka, gwaggo bintu kam tafita tanamai ta6e bakinta.

*6:30am*
     Aysha tashiga d'akin Umma (abokiyar zaman mama), Umma nazaune afalo tana waya Aysha tashigo ta zauna ak'asa tana sharar kwallah.
    Ganin haka Umma takatse wayar tata, takamo hannun Aysha tamik'e, kusada ita ta zaunar da'ita tareda rungumeta, ALLAH Sarki shatu d'iyar albarka, kiyi hak'uri kinji, yazamuyi, haka ALLAH ya tsaramana rabuwa daku badan mun shiryaba, inamiki fatan Alkhairi kinji, kibar kuka tunda kinga nanda wata 1 ma zaku zo bikinsu Hafsat, insha ALLAH zamu kasance masu muku Addu'a aduk inda kuka tsinci kanku, amma kirik'e addininki, kada kiyarda kiyi sakaci dashi, banda biyema shed'anun mutane, kitsare mutuncinki kikula da kanki kinji, ALLAH yabamu hak'urin rashin juna, ALLAH yajik'an Malam.
       Sosai Aysha taji dad'in nasihar Umma, Dan tana kallontane tamkar mama, tanajin dad'in yanda Umma da mama ke zaman lfy, tunda take bata ta6ajin sunyi fad'aba, ko kuma habaici irinna kishiyoyi.
      Gwaggo bintu ce shigo tana fad'in yaya barirah barta mutafi hakanan, nikam ina mamakin son 'ya'ya irin naku, yakamata dai kusama zukatanku salama.
     Umma batace komaiba, Dan tasan bak'ar magana gwaggo bintu tafad'a mata, kuma idan dasabo sun sabaji, Dan kokad'an gwaggo bintu batada kirki, (irin dangin mijinnanne masu d'aukar matan 'yan uwansu da zafi).
        Sudukansu ba k'aunarsu takeba, saidai tafi nuna k'iyayyarta ga Maman Aysha, kasancewar Maman Aysha tanada zafi, bata barin saita kwana, Dan bata ragama gwaggo bintu kokad'an.
      sunaji suna gani gwaggo bintu tad'auke Aysha suka tafi.
   Kukakam sunshashi, barema sa'adiyya da Rufaida, wad'anda suka kasance kusan sa'anni, amma yazasuyi an rabasu da 'yar uwarsu.
     Mama kam k'in fitowama tayi daga d'akinta harsu Aysha suka tafi.

CIKI DA GASKIYA......!!Where stories live. Discover now