51

4.6K 309 0
                                    

51

       A tsakkiyar falon yatsaya, yanamai binsa da kallo daki-daki, komai ya birgesa da k'ayatar dashi, gawani sassanyan k'amshi Na tashi, Wanda akasan duk gidan amarya dashi, yadire ledojin hannunsa Wanda shima baisan miye acikinsuba, Dan youseef ne yabashi.
      Rasa d'akin dazai dosa yayi, baisan ainahin d'akin da matar tasa takeba, yay shiru yana nazarin d'akuna ukku dake cikin corridor d'in, zuciyarsace tafi karkata dana k'arshe, cigaba yayi datakawa ahankali, kaikace yana tsoron Isa ga d'akinne. Harya k'arasa jikin k'ofar.
      Zuciyarsa tashiga harbawa da sauri-da sauri, shikam ba jarumi baneba awannan ga6ar, zai iya rantsuwa baita6a kasancewa dawata mace daba muharramar saba Na tsawon minti talatin, dagashi sai ita, saidai abokan aiki, suma basukad'aiba gaskiya, dolene kasamu akwai wani taredasu.
      Cikin rinmtse ido yamurd'a handle d'in k'ofar yashiga, bashida za6in daya wuce hakan, musamman idan yatuna da lectures d'in malamai data gudana a wajen waleemar auren nasa.
       Sallama yayi amma babu amsa.
 
          Jikin Aysha ne yafara rawa, danjin muryar Wanda batayi zaton ganiba a wannan lokacin, takuma cusa kanta acikin filillukan da aka k'awata kwalliyar gadon dasu, gaba d'aya jitai yau soyayyar datake masa tagudu, sai d'unbin tsoro da firgici dasuka maye gurbinsa.
      Cikin takun nutsuwarsa da jarumtar data zame masa halittar jininsa yak'araso gaban gadon. suduka zuciyoyinsune suka k'ara karfin gudun harbawa, saboda kusanci dasuka samu dajuna.
      Ya d'an lumshe idanunsa, tareda kauda kai daga kallonta, yama rasa ta'ina zai fara?.
     Jinsa tsaye akanta yakuma karyar da jarumtarsa, rauni da d'unbin fargabane kawai keta gudu da bugawar zuciyarta, tsoronta yakuma hauhawar farashi lokacin dataji ya khaleel yazauna abakin gadon, kusa gab da k'afafunta, da'ace zata motsama dolene koyaya ta ta6ashi.
      Wata jarumtace tazo masa alokacin daya tuna da wadda yake tare. Cikin muryarnan tasa, maikad'a hanjin marajjin magana yace, "k! tashi mana".
     Shiru Aysha batako motsaba.
    Yakuma fad'in "bak'ya jinane!!".
Yanda yay maganar ad'an tsawace, amma cikin sanyin murya yasa Ayshan tashi zaune, idanunta nacigaba da zubar da hawaye, tagefen ido tasaci kallonsa, tsoro yasake kamata saboda cin karo da fuskarsa a d'inke, kamar yanda tasanta.
        Shima satar kallon nata yakeyi, yabi zara-zaran yatsun hannunta da kallo, lallen yamata k'yau sosai, daga bak'in har jan, yanda take hawaye saita bashi dariya, yau kam babu bakin rashin kunya, tausayinta yad'anji aransa, dan masu iya magana kance *aure yak'in mata*, amma yasan halin kayarsa, zumace saida wuta.
        Mik'ewa yayi tsaye yana fad'in tashi muje.
    Saida yakai bakin k'ofar sannan Aysha tamik'e da k'yar, bata sameshi a falonba, saikawai tasamu kujera ta zauna, jitake gabad'aya auren yafita aranta.
          Fitowarsace takatse mata tunaninta, saiyanzu tama kwalliyar tasa kallon tsaf, kayan d'azunne ajikinsa, amma yanzu yaje yacire babbar rigar, sai wando da riga y'ar ciki wadda dakad'an tawuce d'uwawunsa, yakuma cire hularma, sai kwantaccen gashinsa, Wanda baicika yawaba saboda askewa dayakeyi, hakama sajensa kwance yake luf, da'alama yad'an kwana biyu bai aske sajen nashiba, yasha gyaran fuska, wadda tafito da ainahin chocolate color d'insa, ya khaleel k'yak'yk'yawane, amma bazaka cedashi k'yawu ajin k'arsheba, komai nasa yana tsaka tsaki, idonsanefa dai ALLAH yabashi masha ALLAH, Dan manyane tubarkallah, ko mace sai haka wajen k'yawun idanu da girma, gasu farare tas, idan ransa ya6acine kawai zakaga sunyi jaa da k'ara fitowa, yanada k'yawun mai k'ayatarwa, Wanda zamu iya cewa kwarjininsane ya kuma fiddo taswurar k'yawun haibar tasa.
       Batasan yak'araso falonba, saimaganarsa taji yana fad'in "k tashi ki d'auka min filet da cup".
        Jikin Aysha amace tamik'e, saidai batasan inane kichin d'inba, amma tayi tsaye takasa tanbamayarsa.
    Tsaf yalura da nufinta, amma saiya shareta yad'auki remote yana k'ok'arin kunna TV.
      ‘‘ya khaleel inane kichin d'in?”.
      Shiru yamata, saida yamula Dan kansa sannan yanuna mata da hannu.
     
Kichin d'in yayima Aysha k'yau sosai, komai atsare gwanin sha'awa, kala biyune kawai a kichin d'in, jaa dakuma Fari, kamar yanda falonta yake, ta d'auki filet da cup tad'ora bisa wani madaidaicin tire tafita.
      Yana zaune inda tabarsa, gabansa taje ta ajiye, ya nuna mata ledojin batareda yayi maganaba.
     Itama bata tankaba tasakko, harzata fara bud'e ledojin yasaka hannu yazare gyalen dake lulu6e da jikinta, saboda kid'ima saida Aysha tajuyo ta kallesa, harara ya sakar mata, tayi azamar janye idanunta da kwallah suka fara taruwa aciki.
      Ta d'auka tabud'e, ledar farko kayan fruit ne aciki, d'ayar kuma gasassun kaji guda hud'u, saikuma d'ayar ledar fresh milk ne aciki.
           Kaza d'aya tasaka a filet d'in tanata tashin k'amshi, tabud'e fresh milk tazuba a cup d'in.
     Tad'ago ido ta kalleshi, ganin idonshi akanta, ta janye nata, tanaso tacemasa tazuba amma takasa magana.
      “Shin waike kinzama kurmane yau?”.
     Kanta ta girgiza masa. Yace, "dabakinki nakeson ki amsa mini, dama Ashe ked'in mara kunyar k'aryace?".
    Itadai bata kulashiba tace, " nazuba maka".
     “kin zuba mana dai, ko kina nufin wad'annan kwala-kwalan idanun naki ba yunwa baceba?”.
      Shiru tayi bata tanka masaba, aranta tace, “dayakema talle bazatama Audi goriba, kaima kanada kwala-kwalan idanun, komawa tayi jikin kujera tayi shiru.
     Shima baisake cewa komaiba yasakko k'asan yazauna kusada ita, yunwa yakeji, rabonsa da abinci tun breakfast dayayi a Kano, fresh milk yad'auka yafarasha da bismillah.
          Saida yasha kusan rabin kofin sannan yacire tareda d'ora kofin kan bakin Aysha, d'ago idanu tayi suka had'a ido, takuma marairaice fuska ALLAH ya khaleel nak'oshi.
    Eh nasan kin k'oshi, nima aibance baki k'oshinba, ina jaddada sunnar manzon ALLAH ne (SAW), Dan haka bismillah.
    Akunyace Aysha tabud'e baki ta kar6a, baicire kofinba daga baki ta saida yaga ta shanye.
    Namanma koda yaci saiya kai baki ta, danma karta masa gardama saiya kuma had'e fuska, duk kunya ta dabaibaye Aysha, amma babu yanda zatayi, dole taita kar6a, ganin zaisata amai tace wlhy nak'oshi ya khaleel.
    Daina bata yayi yana fad'in gulmammiya, dama kinaso kiketa wani dojewa, amare natsoron cin kazar amarci amma ke kincinye guda d'aya sukutum, ammadai kinji kunya gaskiya.
       Aysha batasan sanda murmushi ya su6uce mataba, can k'asan ranta kuma tanajin nishad'i, ya khaleel ya ciyar da ita da hannunsa, batayi zaton samunsa da sauk'i hakaba, ganin halin ko'in kula dayake nuna mata kafin auren Nasu, azatonta kafin auren zata had'a watama bata ganshiba wlhy.
  
       Wringing d'in wayarsane takatse tunanin Aysha, shima cikin matuk'ar mamaki yace, "wanene a darennan haka? Yay maganar yana ciro wayar daga aljihun rigarsa, Momy kuma? to ALLAH yasa dai lafiya? Ya kalli agogon dake tsintsiyar hannunsa sannan yad'aga wayar.
     Maimakon muryar Momy saiyaji ta Anty Zuwairah.
    ‘Khaleel kana gida kuwa?’ tafad'a akid'ime.
    “eh ina gida, amma lfy a darennan?”.
        Babu lafiya khaleel, momyce keta murkususu harda suma cikinta Na ciwo.......
     Da sauri yamik'e yana fad'in, "subahanallah, ganina zuwa", baijira amsartaba ya yanke wayar. Amma zuciyarsa Na mamaki, ganin babu dad'ewa da dawowarau wajen dinner. koda yake ba'a mamaki da ikon ALLAH, saima ta iya mutuwa, wannan kad'an daga ikonsane.
     Aysha tace, “lafiya kuwa?”.
      “momyce babu lafiya, bara nadubo jikin Nata ”.
       To kawai Aysha tace, tareda fad'in, “ALLAH yabata lafiya”.
    Yana tafiya yana amsawa.
Kokad'an batun baikama hankalin Ayshaba, tabbas tasan makircine, saidai tana tsoron kullin nasu.
    Da sauri tamik'e tashiga bedroom d'inta, wayarta tad'auka takira Anty meerah.
    "Lil sholy lfy kuwa da daddarennan? Ina kikabar mijin naki?".
     Yafita wajen Momy.
       Kamarya sholy?.
    Aysha ta zayyane mata komai tana hawaye, tak'are maganar da fad'in Anty meerah wlhy inajin tsoro".
    'Dolene Aysha, Dan tabbas akwai abinda suka shirya, su Anty glo shaid'anune, nasan sun sanarma surukarki komai, yanzu ki kulle ko ina, kuma ki ajiye waya a hannunki, dakinji abinda bai gamshekiba ki kira ya khaleel ki sanar masa'.
    " Anty meerah banida number sa".
       'Babu damuwa, bara nad'auka a wayar dadyn Raudat Na turo miki, ALLAH yasa da ita yake aiki, dannaga waya d'ayace a hannunsa k'aramar Nokia'.
    To amin, baradai Na turo miki.

CIKI DA GASKIYA......!!Where stories live. Discover now